Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Damisa Tayi Wasan Kura A Cikin Wata Makaranta A Kasar India


Tiger iran
Tiger iran

A ranar Lahadi da ta gabata ne, wata damisa ta shiga wata makaranta mai suna “Vibgyor International School” a garin Bangalore kasar India. Damisar dai tayi ma mutane shida rauni, a lokacin da suke kokarin kamata. Duk dai da cewar raunin da ta jimusu ba wai munmunan rauni bane.

An kwashe sama da awowi goma 10, ana kokarin kama wannan damisar, har sai da ta kai an harbeta da wasu allurai da suka kashe mata karfin jiki. Cikin wadanda tajima rauni sun hada da wani masani a harkar kimiyya da fasaha, haka kuma da ma’aikacin gandun daji, sai mai aikin daukar bidiyon yadda abubuwan keta gudana.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jaridar sashen Hausa na gidan radiyon Muryar Amurka (VOA). Dan asalin Hiliya a karamar hukumar Tambuwal, jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG