Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Juventus Zata Fafata Da Barcelona A UCL 2016/2017 Quarter Final


A yau za'a dawo cigaba da karawa a fagen gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai Uefa champion league, na shekara 2016/2017 a matakin wasan kusa da na kusa da na karshe (Quarter final) Inda kungiyar kwallon kafa ta Juventus, zata karbi bakuncin Barcelona, B Dortmund zata barje gumi tsakaninta Monaca, za'a buga wasanne da misalin karfe takwas saura kwata na dare agogon Najeriya, Nijar kamaru da kasar Chadi.

Shekara biyu kenan rabon Juventus, ta hadu da Barcelona, tun bayan karawarsu a wasan karshe na cin kofin zakarun nahiyar Turai a shekara ta 2015, inda Barcelona, ta samu nasarar doke ta da kwallaye 3-1.

A tarihin karawarsu sun hadu sau biyar Barcelona, tayi nasara sau biyu itama Juventus, sau biyu anyi kunnen doki sau daya

Sai karawarsu da zasuyi ta shida a yau.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:27 0:00

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

XS
SM
MD
LG